Advertisement

Responsive Advertisement

An kashe mutane lokacin da aka ƙona ofishin NNPP a Tudun Wada ta jihar Kano

Jam'iyyar NNPP a jihar Kano ta yi zargin cewa an kashe wasu magoya bayanta yayin da aka ƙona ofishin jam'iyyar na Tudun Wada.

Mai magana da yawun NNPP din Sanusi Bature Dawakin Tofa ya ce aƙalla mutum uku ne aka kashe a harin da ƴan APC suka kai ofishin jam'iyyar da yammacin Lahadi. 

Ya ce an kuma jikkata wasu mutane 42 da aka harba da bindiga da kuma waɗanda aka sara. 

To sai dai shugaban jam'iyyar APC a Kano Abdullahi Abbas ya musanta cewa ƴan jam'iyyarsu ne suka kai harin.

Post a Comment

0 Comments