‘Dan takaran Shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya yi zarra a rumfarsa
A akwatin yankin Jada inda Wazirin Adamawa yake zabe, ba a maganar kowa sai jam’iyyar PDP
Bola Tinubu ya samu kuri’a 57, sai Peter Obi da Rabiu Kwankwaso suka zo na uku da na Hudu
Adamawa - Atiku Abubakar mai neman takarar shugabancin Najeriya a karkashin babbar jam’iyyar PDP ya samu galaba a akwatin zabensa.
Jami’in zaben hukumar INEC na rumfar zaben da ke garin Jada, Nalawu Phillip ya tabbatar da cewa Atiku Abubakar ya samu kuri’u 282 a zaben.
Daily Trust ta ce wanda ya zo na biyu shi ne ‘dan takaran jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu. APC da Asiwaju Bola Tinubu sun samu kuri’u 57.
0 Comments