Advertisement

Responsive Advertisement

Obasanjo ya bukaci a soke zaɓen shugaban ƙasa a yankunan da aka yi tashin hankali


 Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce babu nagarta a babban zaɓen ƙasar da aka yi ranar Asabar a don haka ya ce dole ne a soke shi a yankunan da aka yi tashin hankali.

Ya buƙaci Shugaban Hukumar zaɓe ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu da ya ceci Najeriya daga faɗawa haɗarin rikici.

Tsohon shugaban ƙasar ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ya yi wa taken "Zaɓen Shugaban Najeriya na 2023: Rokon A yi taka tsan-tsan da kuma gyara.''

Obasanjo ya ce ba wani abin sirri ne, cewa an zargi wasu daga cikin ma'aikatan hukumar zaɓen da suka gudanar da aikin sun bayar da kai sakamakon aika alkaluman zaɓen ba ta hanyar na'ura ba, abin da ya sa ake zargin wani sakamkon an ƙirƙire shi ne.

Post a Comment

0 Comments