Advertisement

Responsive Advertisement

PDP ta yi ƙorafi kan sakamakon zaɓen Ekiti


 Wakilin jam'iyyar PDP a dakin tattara sakamakon zaben shugaban ƙasa, Sanata Dino Melaye ya yi ƙorafin cewa an tafka maguɗi a sakamakon zaɓen shuagaban ƙasa na jihar Ekiti.

Dino Melaye ya yi ƙorafin a gaban shugaban hukumar zaɓe farfesa Mahmood Yakubu, inda ya ce INEC ta sake duba batun kuri'un jihar. 

Melaye ya kuma yi korafin cewa INEC ba ta saka sakamakon zaɓe a cikin rumbun bayananta na intanet.

Sai dai, farfesa Yakubu ya mayar da martanin cewa alkaluma da wakilin na PDP ya bayyana hukumar bata san da su ba saboda waɗanda ke hannunta sahihahi ne.

Jam'iyyar PDP ta ce hukumar INEC ta saba wa doka wajen rashin sanya sakamakon zaben shugaban kasa a manhajarta ta intanet.

Post a Comment

0 Comments