Advertisement

Responsive Advertisement

Wike Ga Ribas: Ba Zan Muku Kuskuren Zaben Ɗan Takarar Shugaban Kasa Ba


 Gwamna Wike ya ja hankalin mutanen jihar Ribas da cewa ba zai yaudare su ba game da wanda zasu zaba ranar Asabar Nyesom Wike,

jagoran gwamnonin G-5 sun raba gari da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyarsa PDP, Atiku Abubakar 

A halin yanzun ana jiran aga wane ɗan takara mazauna Ribas zasu zaba tsakanin manyan masu neman gaje Buhari 

Rivers - Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya faɗawa mutanen jihar cewa su aminta da shi game da ɗan takarar shugaban kasan da zasu jefa wa kuri'unsu ranar Asabar. 

Gwamnan ya jaddada cewa tuni masu ruwa da tsaki suka ɗauki wanda ya cancanta Ribas ta tula wa kuri'unta kuma sun bi matakan da ya dace wajen zaɓen.

Wike ya ce ba zai wa mutanensa zaɓen tumun dare ba kuma ya sake nanata cewa zai ci gaba da fafutukar kare muradan mazauna jihar Ribas duk rintsi kuma a ko wane lokaci.

The Nation ta rahoto cewa Nyesom Wike ya yi wannan jawabin ne yayin kaddamar da wasu muhimman ayyukan titi a yankin ƙaramar hukumar Patakwal ranar Alhamis.

Post a Comment

0 Comments