Advertisement

Responsive Advertisement

Ƴan Najeriya za su yi kewar Buhari idan ya sauka daga mulki – Garba Shehu



 Babban mai bai wa Shugaban Najeriya shawara kan kafafen yaɗa labarai, Mallam Garba Shehu ya koka kan irin caccakar da ake yi wa shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari.

Ya ce ba a nuna ƙauna ga shugabanni a lokacin da suke mulki.

Ya bayar da misali da zamanin mulkin Goodluck Jonathan wanda ya ce mutane sun yi ta sukarsa amma a yanzu, ya zama mutumin da ƴan Najeriya da dama ke yabo.

Mallam Garba Shehu ya ce irin haka za ta faru idan Buhari ya miƙa mulki ga shugaban ƙasa na gaba.

Game da manufar taƙaita amfani da garin kuɗi, Garba Shehu ya ce tsarin na gwamnati mai ci abin so ne a don haka ba za a soke shi ba.

A cewarsa, "taƙaita amfani da takardun kuɗi ci gaba ne ga ƴan Najeriya saboda ƙasashen da suka ci gaba tuni suke tafiya a kan wannan tsarin".

Al'ummar Najeriya sun yi ta fuskantar matsaloli saboda ƙaranvin takardun kuɗi tun bayan da gwamnati ta bijiro datsarin sauya fasalin takardun kuɗin.

Post a Comment

0 Comments