Advertisement

Responsive Advertisement

Dillalan Man Fetur Sun Ki Batun Karbar Tsoffin Takardun Naira Duk da Umarnin CBN


 Kungiyar dillalan man fetur ta IPMAN ta bayyana rashin amince da kashe tsoffin kudi duk da umarnin kotu da na CBN 

Wannan na zuwa ne a ranar Litinin, inda aka tattauna da wani shugaban kungiyar kan matsayarta a wannan karon 

Tun bayan kawo batun sauyin Naira, an sha samun cece-kuce da sabani tsakanin ‘yan Najeriya da bankunan kasar nan 

Najeriya - Dillalan man fetur a ranar Litinin sun ci gaba da bayyana rashin amincewarsu da karbar tsoffin takardun Naira daga hannun mutane, duk da cewa CBN ya ba da umarnin a ci gaba da karbar kudin. 

An kuma tattaro cewa, har yanzu bankuna basu yi magana da dillalan mai da masu gidajen mai ba game da ci gaba da karbar tsoffin kudin a Najeriya, Punch ta ruwaito.

Post a Comment

0 Comments