Gwamna Wike na jihar Ribas ya kara durkusad da jam'iyyar APC yayin da ake dab a zaben gwamna ranar Asabar
A ranar Talata 7 ga watan Maris, Wike ya karbi wasu gungun mambobin APC da suka sauya sheka zuwa PDP
A cewar jagoran tawagar yan siyasan, sun zabi shiga PDP ne domin jawo wa yankinsu ayyukan ci gaba
Rivers - Gwamnan Ribas, Nyesom Wike, ya jaddada cewa babu tantama Peoples Democratic Party (PDP) ce zata lashe zaben gwamna da mambobin majalisar dokokin jihar.
Wike ya yi wannan furucin ne ranar Talata yayin da yake karɓan dandazon mambobin APC da suka sauya sheka zuwa PDP a ƙaramar hukumar Ahoada ta gabas.
0 Comments