Advertisement

Responsive Advertisement

INEC ta saka ranar ƙarasa zaɓukan da ba a kammala ba


 Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC ta sanya ranar Asabar 15 ga watan Afrilu a matsayin ranakun da za ta kammala zaɓukan da ba a ƙarasa ba a ƙasar.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce ta yanke shawar ne bayan wata ganawa da ta yi da jami'an hukumar.

Hukumar ta ce sai a ranar Asabar 15 ga watan Afrilun ne za a ƙarasa zaɓukan gwamnoni da na 'yan majalisun dokokin da ba a karasa ba, sakamakon wasu matsaloli.

Hukumar zaɓen ƙasar dai ta ayyana zaɓukan gwamnonin jihohin Adamawa da Kebbi a matsayin wanda bai kammala ba.

Post a Comment

0 Comments