Jiga-jigan jam’iyyar PDP a jihar Katsina sun bayyana sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulkin jihar gabanin zaben gwamnoni
Jam’iyyar ta APC ta bayyana jin dadi da kuma gwarin gwiwar cin zabe a irin wannan lokaci na nasarar samun sabbin mambobi
Ana ci gaba da shirin zaben gwamnoni a Najeriya, a ranar 11 ga watan Maris ne za a yi zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi
Jihar Katsina - Jam’iyyar APC a jihar Katsina ta karbi manyan mambobin jam’iyyar PDP bakwai da magoya bayansu sama da 10,000 a ranar Talata.
Da yawan wadanda suka sauya shekan sun kasance na kusa da tsohon gwamnan jihar, Alhaji Ibrahim Shema, inji rahoton PM News.
0 Comments