Advertisement

Responsive Advertisement

Mene ne hukuncin ɗanɗana abinci ga mai azumi?


Azumin Ramadan lokaci ne da al'ummar Musulmi a faɗin duniya ke zage damtse don yin ayyukan da za su inganta imaninsu tare da kyautata wa ƴan uwa da abokan arziki duk domin neman tsira da samun lada.

Ɗaya daga cikin abubuwan kyautatawa da ke ƙara yawan lada a wannan lokaci shi ne ciyarwa kuma bisa al'ada, mata a gidaje sukan yi tanadi don girka abinci iri-iri da nufin faranta ran mai gida da ƴaƴa har ma da abokan arziki.

Sai dai a lokacin dafa abincin buɗa-baki, wasu mata kan yi shakku wajen tabbatar da ko ɗanɗanon girkinsu ya yi daidai, kasancewar yanayin azumi da suke ciki.

BBC ta tuntuɓi Malaman addinin Musulunci don jin hukuncin ɗanɗana abinci a yayin azumi.


Malama Fatima Laminu, wata malamar addinin Musulunci a Abuja, ta ce babu laifi idan aka ɗanɗana abinci matuƙar "mutum ba zai bari yawun ya wuce zuwa maƙogwaronsa ba."

Ta ce sai dai yin hakan na iya zama kuskure idan aka yi da ganganci har abincin ya wuce maƙogwaro, wanda idan hakan ta faru, toh ya zama dole mutum ya rama azumi.

Ta ce hanya mafi sauƙi ga mai azumin da ke son ɗanɗana girki, ita ce ya furzar da duk abin da ya ɗanɗana kafin ya tafi cikin maƙoshi.

Sai dai ta ce an samu saɓani tsakanin malamai game da mai azumin da ya ɗanɗana abinci har ya wuce maƙogwaro, amma ba da saninsa ba.

A cewar Malama Fatima, "wasu malaman sun ce, mutum zai kai azumin sannan kuma ya rama, wasu kuma sun ce tun da kuskure ne, in dai a kan mantuwa ne, ba abin da ya samu azuminsa, wato dai azuminsa yana nan."


 

Post a Comment

0 Comments