Advertisement

Responsive Advertisement

Saudiyya ta ƙwace tan biyar na naman kaji da ya lalace


 Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Saudiyya (SFDA) ta ƙwace tan biyar na naman kajin da ya lallace a wani gidan ajiye kayyakin abinci da ke birnin Riyadh.

Hukumar ta tabbatar da cewa gidan ajiyar kayan abincin ya saɓa wa ƙa'idoji masu yaw, cikin har da yin ƙarya sayar da kayayyakin da suka lalace, inda ake sake wa naman kajin mazubi tare da sanya musu sabbin kwanan watan lalacewa.

Haka kuma hukumar ta ce gidan ajiyar ya saɓa wa dokokin lafiya, da amfani da ma'aikatan da ba su da takardun shaidar karatun lafiya.

SFDA ta kuma rufe gidan ajiyar tare da lalata duk kayyakin da ta ƙwace.

Hukumar ta ce ta gudanar da wannan aiki ne tare da hadin gwiwwar hukumar gudanarwar birnin Riyadh da ma'aikatar kasuwanci da ma'aikatar walwala da ci gaba jama'a da hukumar zakka da haraji ta ƙasar tare kuma da hukumar fasa ƙwauri ta ƙasar.

Haka kuma hukumar ta yi kira ga kwastomomi da su kai rahoton duk wani shago ko kamfanin da ya sayar musu da kayayyakin da suka lalace.

Post a Comment

0 Comments