A wata sanarwa da rundunar ta fitar ofishin hukumar da ke yankin unguwar Apo a babban birnin tarayyar ƙasar ya samu ƙorafi daga wata mata da ke zaune a unguwar.
Inda ta yi zargin cewa makwabcinta yana yi wa 'yarta fyaɗe.
Nan take kuma rundunar ta kai samame tare da kama mutumin, inda bayan da aka tuhume shi, ya rubuta da kansa cewa ya sha yin lalata da yarinyar.
A yanzu dai yarinyar mai shekara 10 na asibiti, inda ake kula da lafiyarta.
Kwamishinan 'yan sandan birnin tarayyar CP Sadiq Idris Abubakar ya yi kira da iyaye da su riƙa lura sosai a kan 'ya'yansu da mutane da ke kewaye da su, tare da ɗaukar matakan da suka dace don magance yawaitar fyade a cikin al'umma.
0 Comments