1. Uba Sani Uba Sani shi ne ‘Dan takaran Gwamnan jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar APC. Sanatan mai shekara 52 zai zo ya zama magajin mutuminsa, Nasir El-Rufai.
Asalinsa mutumin Zariya ne, kuma ya yi digirinsa a bangaren Injiniyanci, daga baya ya yi digirgir a fannin tattalin arziki da PGD a kasuwanci a Kalaba da Abuja
2. Rt. Hon. Isa Ashiru Kudan Hon. Isa Ashiru Kudan yana neman kujerar Gwamnan Kaduna a jam’iyyar PDP. An haifi Sarkin Ban Zazzau ne a 1962, ya yi karatunsa tsakanin Kaduna da Kano.
Isa Ashiru Kudan ya samu Difloma a 1985 a harkar kula da kasuwanci, a 1989 ya yi nasarar samun babbar difloma, yana da shaidar Digirgir daga jami’ar BUK a 2001.
0 Comments