Advertisement

Responsive Advertisement

'Za mu yi aiki har da 'yan adawa domin ciyar da Katsina gaba'


 A Najeriya, zababben gwamnan jihar Katsina Dikko Umaru Radda karkashin jam'iyyar APC mai mulki, ya ce gwamnatinsa za tayi aiki da kowanne bangare na al'umma domin tabbatar da ta ciyar da jiharsa gaba.

Radda ya ce abun da zai maida hankali akai shi ne ciyar da Katsina gaba da kawo sauyte say

Dikko Umaru Radda ya kuma ce ya yi mamaki wasu zarge-zarge da batutuwan da suka biyo bayan zaben da ya bashi nasara, sai dai kuma ba shi da wata fargaba domin ya san al'umma jihar Katsina ne suka zabe shi, saboda gamsuwa da manufofinsa.

Kan batun 'yan adawa musamman jam'iyyar PDP da Sanata Yakubu Lado Danmarke ya yi zargin an tafka magudi da aringizon kuri'u a lokacin zaben gwamnan da aka yi ranar 18 ga watan Mayu, da shan alwashin daukar matakin shari'a, Dikko Radda ya ce ba ya ko dar domin ya san an yi sahihin zabe a jihar Katsina.

Post a Comment

0 Comments