Advertisement

Responsive Advertisement

Zaɓen Najeriya: Nazari kan ƙorafin ƴan hamayya game da zaɓen da aka yi wa Bola Tinubu


 


An bayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya bayan wata fafatawa mai zafi, sai dai wasu da dama ciki har da 'yan takarar shugaban ƙasar da suka fafata da shi, kan cewa an yi maguɗi.

Sun yi kira da a soke duka zaɓen, suna zargin cewa Hukumar Zaɓe, INEC, ta karya dokar tattara sakamakon zaɓen saboda ta taimaka wa Tinubu.

INEC ta musanta wannan zargi haka kuma jam'iyyarsa ta APC.

Ta ɓangaren jam'iyyun hamayya har yanzu ba su gabatar da wata ƙwakƙwarar hujja ba kan zarge-zargensu.

Post a Comment

0 Comments