An bayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya bayan wata fafatawa mai zafi, sai dai wasu da dama ciki har da 'yan takarar shugaban ƙasar da suka fafata da shi, kan cewa an yi maguɗi.
Sun yi kira da a soke duka zaɓen, suna zargin cewa Hukumar Zaɓe, INEC, ta karya dokar tattara sakamakon zaɓen saboda ta taimaka wa Tinubu.
INEC ta musanta wannan zargi haka kuma jam'iyyarsa ta APC.
Ta ɓangaren jam'iyyun hamayya har yanzu ba su gabatar da wata ƙwakƙwarar hujja ba kan zarge-zargensu.
Sai dai ɗan takarar jam'iyyar Labour Peter Obi wanda ya zo matsayi na uku a zaɓen ya ce, zai je kotu domin a ƙwace nasarar da Tinubu ya samu, saboda a cewarsa tasa ce. Amma shi kansa babu wata hujja da ya gabatar.
Abin da ake ta rikici a kansa shi ne na'urar da aka gabatar domin karɓar sakamakon zaɓen wadda ake kira BVAS, wadda aka yi tsammanin za ta sauƙaka maguɗin zaɓen da ake yi a zaɓen Najeriya, ya kuma sanya zaɓen ya zama mai sahihanci.
Ƙorafe-ƙorafen da ake yi na cewa ma'aikatan hukumar sun gaza tura sakamakon zaɓen daga rumfunan zaɓensu zuwa rumbun tattara zaɓe na INEC, wanda hakan ya janyo ƙorafin cewa kamar da haɗin bakin hukumar domin a yi maguɗi.
0 Comments