Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bai wa al'ummar ƙasar tabbacin sadaukar da kansa ga hidimta wa jama'a iya ƙarfinsa.Ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar bayan da hukumar zaɓen Najeriya ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2023.
Gogaggen ɗan siyasar mai shekara 70, ya samu kashi 36 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa kamar yadda sakamakon da aka sanar a hukumance ya nuna.
A jawabin nasa, zaɓɓen shugaban ƙasar ya yi wa ƴan Najeriya alƙawarin cewa mulkinsa zai kawo zaman lafiya da haɗin kai da kuma ci gaba kuma nan gaba idan mutane suka duba ci gaba n da suka samu, za su yi alfahari da kasancewarsu ƴan Najeriya.
Ya yi alƙawarin zama shugaba mai adali da zai mutunta buƙatun jama'a tare da yin ƙoƙari wajen gina Najeriyar da kowa zai yi alfahari da ita.
Ya ce "Ina cikin farin ciki na zaɓa ta da kuka yi a matsayin shugan Najeriya na 16 domin hidimtawa jamhuriyarmu da muke ƙauna. Wannan wani lokaci ne na haskakawar kowanne mutum da kuma ƙara tabbatar da dimokraɗiyyarmu. Ina muku godiya,"
Da take magana kan abokan takararsa da suka fafata a zaɓen, Tinubu ya bayyana cewa yanzu ne lokacin da za su haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gina ƙasar tare.
"Ko magoyin bayan Bola Ahmed Tinubu ne ko Atiku ko Obi ko Kwankwasiyya ko kuma wani ɓangare na siyasa, na san ka yi zaɓe ne domin ci gaban Najeriya da kyakkyawan fata ga ƙasar, ina muku godiya saboda nuna sadaukarwa ga dimokraɗiyyarmu,"
"Kun miƙa yardarku da amincewa kan burin da Najeriya ke da shi na dimokraɗiyya domin ciyar da ita gaba da kuma tunanin samun haɗin kai, da adalci da zaman lafiya da haƙuri da juna. Sabunta kwarin giwa ya tabbata a Najeriya.
Bola Tinubu ya kuma yaba wa INEC saboda gudanar da zaɓe mai adalci. A cewar shi, "Kurakuran da aka samu na da alaƙa da wasu lambobi ne da basu da yawan da za su lalata sakamakon ƙarshe na zaɓen. A kowanne mataki na zaɓukan, mun amince da duka ayyukan da aka yi da suke da muhimmanci da rayuwar dimokraɗiyyarmu."
0 Comments