Advertisement

Responsive Advertisement

Zan gina Najeriya mai nagarta – Bola Tinubu


 Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bai wa al'ummar ƙasar tabbacin sadaukar da kansa ga hidimta wa jama'a iya ƙarfinsa.

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar bayan da hukumar zaɓen Najeriya ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Gogaggen ɗan siyasar mai shekara 70, ya samu kashi 36 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa kamar yadda sakamakon da aka sanar a hukumance ya nuna.

A jawabin nasa, zaɓɓen shugaban ƙasar ya yi wa ƴan Najeriya alƙawarin cewa mulkinsa zai kawo zaman lafiya da haɗin kai da kuma ci gaba kuma nan gaba idan mutane suka duba ci gaba n da suka samu, za su yi alfahari da kasancewarsu ƴan Najeriya.

Post a Comment

0 Comments