Saudiyya ta kammala shirin duban watan sallah a daidai lokacin da al'ummar Musulmi suka ɗauki azumi na 29.
Shafin Masallacin Harami na Makka da Madinah ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa daga yau Alhamis za a fara duban watan na Shawwal.
An girke manyan na'urorin hangen nesa domin aikin duban watan Shawwal.
Ana sa ran fara duba watan Shawwal ne a birnin Sudair da misalin ƙarfe 06:09na yamma, sai garin Tumair inda za a fara duba da 06:22na dare.
A Najeriya ma, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar III ya bukaci al'umma su fara duban jaririn watan Shawwal daga yau Alhamis 29 ga watan Ramadan.
0 Comments