Advertisement

Responsive Advertisement

Ƙananan jam'iyyu sun ce sun gamsu da yadda INEC ke karɓar sakamakon zaɓe


 Wasu ƙananan jam'iyyun siyasa a Najeriya sun ce sun gamsu da yadda hukumar INEC take gabatar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da ke gudana a zauren tattara sakamakon zaɓen.

Tuni dai wasu jam'iyyu ciki har da manyan jam'iyyun Adawa PDP da LP, suka fice daga zauren bayan da suka yi ƙorafin cewa INEC ba ta ɗora sakamakon zaɓen a shafinta na intanet ba.

Ƙananan jam'iyyun sun bayyana matsayarsu ne a matsayin martani kan ficewar da manyan jam'iyyun hamayya PDP da LP da wasu jam'iyyun suka yi daga zauren da ake kaɓar sakamakon zaɓen shugaba ƙasa a Abuja.

Jam'iyyun da suka fice sun nuna rashin gamsuwa da yadda INEC ke karɓar sakamako daga jihohi.

Sun nemi lallai INEC ta tabbatar an sanya sakamakon zaben a shafin intanet na hukumar zaɓen kamar yadda INEC ɗin ta alƙawarta yi tun da farko.

Wakillan ƙananan jam'iyyun sun tashi ɗaya bayan ɗayan a zauren cibiyar tattara sakamakon inda suka nesanta kansu daga ficewar jam'iyyun na hamayya.

Wasu daga cikin Jam'iyyun da suka ce suna tare da INEC sun haɗar da PRP da APP da BP da NRM da YPP da AAC da AA da AP da kuma jam'iyyar NNPP.

Ita ma jam'iyyar APC mai mulki wacce kawo yanzu ita ce kan gaba a sakamakon da INEC ta karɓa ta ce ta gamsu da yadda hukumar zaɓen ke karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasar.

Post a Comment

0 Comments