Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya jinkirta shirin gwamnatinsa na yi wa tsarin shari'ar kasar garanbawul mai cike da cece-kuce har zuwa zaman majalisa na gaba.
Ya ce kasar na fuskantar rikicin da ke barazana ga hadin kan kasa.
An dai gudanar da zanga-zanga a sassan kasar tare dayajin aikin domin adanawa da sauyin .
Tun farkon wannan shekara, mutane suka fara haɗa manya-manyan zanga-zanga ta mako-mako domin nuna adawa da shirin gwamnati na kawo sauyi a wasu tsare-tsarenta.
Zanga-zangar ta yi ta yaɗuwa, inda dubban ɗaruruwan mutane suka mamaye titunan Tel Aviv - birnin kasuwancin ƙasar - da kuma da wasu birane da garuruwa a faɗin ƙasar.
Masu zanga-zanga sun yi kira da a soke shirin kawo sauyi da Firaminista Benjamin Natenyahu ke son yi, inda suka bukaci da ya sauka daga mulki. Ƴan adawarsa na siyasa su ke jagorantar zanga-zangar, ko da yake tsananin adawa da sauye-sauyen ya kasance cikin ƴan siyasa.
Wasu sojoji ma da suka kasance kashin bayan sojojin Isra'ila - sun nuna adawarsu da sauyin ta hanyar kin zuwa aiki, inda hakan ya ƙara nuna fargabar da ake da ita na cewa yanayi tsaron ƙasar na cikin barazana.
0 Comments