Advertisement

Responsive Advertisement

Tuni dubban 'yan kasar da ma kasashen waje suka fice a sanadiyyar fadan da ya barke sama da mako biyu da ya gabata

 

Rikicin Sudan zai fitar da mutum sama da dubu 800 daga ƙasar - MDD

Sudan

ASALIN HOTON, AFP VIA GETTY IMAGES

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa mutane sama da dubu dari takwas ka iya tserewa daga Sudan sakamon kazamin fadan da ake yi tsakanin bangarorin soji biyu da ke gaba da juna.

Ana ci gaba da gwabza fada a babban birnin kasar Khartoum duk da alkawarin dakatar da bude wuta tsakanin bangarorin biyu.

Tuni dubban 'yan kasar da ma kasashen waje suka fice daga kasar ta gabashin Afirka.

Kazamin fadan wanda ya barke tun sama da mako biyu da ya gabata tuni daman ya riga ya haifar da kwararar dubban ‘yan kasar ta Sudan zuwa kasashe makwabta da suka hada da Masar da Chadi da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka.

Haka suma ‘yan kasashen waje gwamnatocin kasashensu da sauran hukumomi na ci gaba da kokarin kwashe su daga kasar, inda tuni suma dubbai suka fice .

A wani taron manema labarai kakakin ma’aikatar harkokin kasashen waje ta Amurka Vedant Patel, ya ce Amurkawa sama da 700 da ‘yan wasu kasashen aka kwashe ta tashar jirgin ruwa da ke garin Port Sudan a cikin kwana ukun da suka gabata, inda yawan Amurkawan da ake fitarwa daga kasar ya karu tun lokacin da aka fara rikicin.

Ya ce; ''A kokarin hadaka na kasashe, gwamnatin Amurka da hadin gwiwar kawayenta da abokan hadin gwiwa ta fitar da ‘yan Amurka sama da 1,000 daga Sudan tun lokacin da aka fara tashin hankalin.''

Post a Comment

0 Comments