Advertisement

Responsive Advertisement

An raunata ƴan sandan Faransa fiye da 100 a gangamin ranar ma'aikata


 Ma'aikatar cikin gida a Faransa ta ce kimanin ƴan sanda 108 ne suka jikkata sanadin arangamar da ta kaure a sassan ƙasar inda masu zanga-zanga ke nuna fushinsu kan sauye-sauyen da aka yi wa tsarin pensho.

Gerald Darmanin ya ce ba kasafai aka cika samun irin haka ba - ƴan sanda da dama su ji rauni. Ya ƙara da cewa an kama mutum 291 yayin tashin hankalin.

Dubban jama'ar ƙasar ne suka shiga gangamin ranar Ma'aikata domin nuna adawarsu da sauye sauyen da Shugaba Emmanuel Macron ya yi.

Akasarin gangamin an yi shi lami lafiya amma an samu wasu masu tsatsauran ra'ayi da suka riƙa wasan wuta. Ƴan sanda kuma sun mayar da martani ta hanyar wulla hayaƙi mai sa hawaye da yi musu feshin ruwa.

Zuwa yanzu ba a tantance adadin mutanen da suka ji rauni ba.

Wannan ne gangami na baya-bayan nan da aka yi kan ɗaga shekarun fara karɓar pensho daga 62 zuwa 64. Ƙungiyoyin ƙwadago na son a janye matakin.

Post a Comment

0 Comments