Advertisement

Responsive Advertisement

Canjin kuɗi : Har yanzu jama'a na shan baƙar wahala a Najeriya


 Jama'a a Najeriya na ci gaba da fuskantar wahala ta samun takardun kudi a bankuna duk da alkawarin da babban bankin kasar ya yi cewa kudaden za su wadata daga ranar Alhamis 23 ga watan nan na Maris.

A ranar Laraba ne babban bankin, ya umurci bankuna da su je rassan CBN na jihohi su karbi tsofaffin takardun kudaden da suka ajiye don saukaka wa jama’a matsalar karancin kudin da ake fama da ita.

Ana ganin babban bankin ya bayar da wannan sanarwa ne bayan da kungiyar kwadago ta kasar NLC ta yi barazanar mamaye dukkanin ofisoshin bankin da ke jihohi ciki har da Abuja domin tilasta wa gwamnati ta dauki matakin na saukaka wa jama'a halin da ake ciki.

NLC ta ce daga mako mai zuwa ne za ta mamaye ofisoshin bankin domin hana su gudanar da ayyukansu.

Post a Comment

0 Comments