Advertisement

Responsive Advertisement

Ko za a iya soke sakamakon zaɓen Najeriya?


 Jam'iyyun adawa a babban zaben Najeriya da aka fafata a kai za su yi kokarin yin abin da za a iya cewa bai taba yiwuwa ba - shi ne samun wata kotu ta soke sakamakon zaben shugaban kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka.

Peter Obi da Atiku Abubakar an takarar da suka zo na biyu da na uku a zaben sun lashi takobin zuwa kotu domin kalubalantar zaben da aka yi yi wa Bola Tinubu na jam'iyya mai mulki ta APC wanda ya sami kashi 37 cikin 100 na dukkan kuri'un da aka kada.

Sai dai wace hujja suke da ita, kuma suna iya sa a soke wannan sakamakon zaben kuwa?

Wane lokaci jam'iyyun siyasa ke da shi na shigar da kara?

Tilas a shigar da kararrakin zabe a Najeriya cikin kwanaki 21 bayan da aka sanar da sakamakon zaben, in ba haka ba, kotuna za su yi watsi da su.

Saboda haka Peter Obi da Atiku Abubakar na da daga yanzu zuwa ranar 31 ga watan Maris ke nan.

Sai dai wannan jan aiki ne ganin cewa sai 'yan takarar sun tattaro bayanai da shaidu daga mazabu fiye da 176,000 da kuma cibiyoyin tattara bayanai fiye da 8,000 na wuraren da aka kada kuri'u da tattara sakamakon a fadin Najeriya cikin wadannan takaitattun kwanakin. 

Wane lokaci kotu ke dauka kafin a bayyana hukunci?

An samar da kwanaki 180 bayan an shigar da kara ga kotunan da ke sauraren kararrakin zabe, kuma ganin cewa Mista Obi da Alhaji Abubakar kowannensu zai shigar da tasa karar ce daban da ta daya dan adawar, daga karshe kowannensu zai sami nasa hukuncin ne a lokacin da kotun da ya tunkara ta kammala sauraren kararsa.

Sai dai idan 'yan takarar biytu ba su gamsu da hukuncin da kotunan sauraren karar zaben suka yanke ba, suna iya daukaka kara zuwa kotun kolin kasar.

Daukaka karar na iya kai tsawon kwanaki 60, saboda haka za a aiya kammala shari'ar cikin watanni takwas ke nan.

Post a Comment

0 Comments