Advertisement

Responsive Advertisement

Haɗarin da ke tattare da siyasar ubangida a Najeriya


 Wasu masana siyasa a Najeriya, sun ce har yanzu siyasar ubangida na tasiri a kasar musamman idan aka yi la’akari da abubuwan da suka gudana a zabukan da aka yi kwanan nan.

Masanan sun ce, siyasar ubangida ta yi tasiri kwarai da gaske a zaben gwamnoni musamman a jihohin Kano da Sokoto inda wasu tsofaffin gwamnoni da suka bar karagar mulki shekaru takwas da suka gabata suka nuna cewa har yanzu suna jan zarensu a siyasar jihohin.

Dr Abubakar Kari, masanin siyasa a jami`ar Abuja, ya shaida wa BBC cewa, a wasu lokutan idan aka yi rashin sa`a irin wannan siyasar tana da tata illar.

Malamin ya ce: “Ba kasafai dangantaka irin ta dasawa ke dorewa tsakanin ubangida da yaran gidan nasu ba, kuma ko da ta dore watakila a yi zama irin na hadin-bauta.”

Post a Comment

0 Comments